unfoldingWord 34 - Yesu ya Koyar da Wassu Labaru

unfoldingWord 34 - Yesu ya Koyar da Wassu Labaru

Outline: Matthew 13:31-46; Mark 4:26-34; Luke 13:18-21;18:9-14

Script Number: 1234

Language: Hausa

Audience: General

Genre: Bible Stories & Teac

Purpose: Evangelism; Teaching

Bible Quotation: Paraphrase

Status: Approved

Scripts are basic guidelines for translation and recording into other languages. They should be adapted as necessary to make them understandable and relevant for each different culture and language. Some terms and concepts used may need more explanation or even be replaced or omitted completely.

Script Text

Yesu ya fadi wadansu labaru da yawa game da Mulkin Allah. Misali, yace, "Mulkin Allah kamar kwayar mastad ya ke da wani ya shuka a gonarsa. Kun sani cewa kwayar mastad ita ce mafi kankanta dukka cikin iri."

"Amma sa'anda kwayar mastad ya girma, sai yafi dukkan itatuwan dake gona girma, kuma da girma sosai harma tsuntsaye sukan zo su huta a cikin rassan sa."

Yesu ya sake fadin wani labari, "Za'a kwatanta mulkin Allah da yistin da mace ke kwabawa cikin curin gurasa har sai ya mamaye dukka curin."

Haka kuma mulkin Allah kamar dukiya ce da wani ya boye a wani fage. Wani mutum dabam ya sami dukiyar shi ma ya sake binne ta. Yana cike da murna harma ya je ya sayar da dukkan mallakar sa, ya yi amfani da kudin don ya sayi filin."

"Haka kuma mulkin Allah kamar lu'u lu'u ne mai darajar gaske. Sa'anda dillalin lu'u lu'u ya same ta, sai ya sayar da dukkan mallakar sa ya yi amfani da kudin domin ya saye ta.''

Sa'annan Yesu ya fadi wani labari wa mutane da suke dogara da ayyukan su nagari amma su na raina sauran mutane. Yace, "Mutane biyu suka je haikali don su yi addu'a. Daya mai karbar haraj i ne, dayan kuma shugaban addini ne."

"Shugaban addinin yayi addu'a kamar haka, 'Na gode maka Allah, domin ni ba mai zunubi bane kamar sauran mutane, barayi, marasa adalci, mazinata, ko kuma kamar wancen mai karban haraji.'''

'''Misali, na kan yi azumi sau biyu ko wace mako, nakan kuma baka daya bisa goma cikin dukkan kudi da kayayyakin da na karba."'

"Amma mai karbar harajin ya tsaya nesa da shugaban addini, baya ma duban sama. A maimakon haka, ya dunkula hannu yana buga girjinsa ya yi addu'a, 'Allah, yi mani jinkai domin ni mai zunubi ne.'''

Sai Yesu yace, "Gaskiya nake gaya maku, Allah ya ji addu'ar mai karban harajin nan ya kuma ce da shi adali. Amma bai so addu'ar shugaban addinin nan ba. Allah zai kaskantar da duk mai fahariya, ya kuma daukaka duk wanda ya kaskantar da kansa."

Related information

Words of Life - Audio gospel messages in thousands of languages containing Bible based messages about salvation and Christian living.

Free downloads - Here you can find all the main GRN message scripts in several languages, plus pictures and other related materials, available for download.

The GRN Audio Library - Evangelistic and basic Bible teaching material appropriate to the people's need and culture in a variety of styles and formats.

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons

Choosing the right audio or video format - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?