unfoldingWord 48 - Yesu Shine Almasihun da aka yi Alkawarinsa

unfoldingWord 48 - Yesu Shine Almasihun da aka yi Alkawarinsa

Outline: Genesis 1-3, 6, 14, 22; Exodus 12, 20; 2 Samuel 7; Hebrews 3:1-6, 4:14-5:10, 7:1-8:13, 9:11-10:18; Revelation 21

Script Number: 1248

Language: Hausa

Audience: General

Genre: Bible Stories & Teac

Purpose: Evangelism; Teaching

Bible Quotation: Paraphrase

Status: Approved

Scripts are basic guidelines for translation and recording into other languages. They should be adapted as necessary to make them understandable and relevant for each different culture and language. Some terms and concepts used may need more explanation or even be replaced or omitted completely.

Script Text

Sa'anda Allah ya hallici duniya, kome na da kyau. Babu zunubi. Adamu da Hauwa'u na kaunar juna, kuma suna kaunar Allah. Babu cuta ko mutuwa. Hakkan nan Allah yake so duniya ta kasance.

Shaitan yayi magana tawurin macijin acikin gonar domin ya rudi Hauwa'u. Sai ita da Adamu suka yi wa Allah zunubi. Domin sun yi zunubi, kowa aduniya yana rashin lafiya kuma kowa na mutuwa.

Saboda Adamu da Hauwa'u sun yi zunubi, wani abin da ya fi wannan muni ya faru. Suka zama makiyan Allah. Sakamakon haka, tun daga lokacin nan kowane mutum an haife shi da dabi'ar zunubi kuma ya zama makiyin Allah. Dangantaka tsakanin Allah da mutane ta yanke saboda zunubi. Amma Allah yana da shirin maido da wannan dangantakar.

Allah yayi alkawari cewa daya daga cikin zuriyar Hauwa'u zai murkushe kan shaidan, shaidan kuwa zai yi wa diddigen sa rauni. Wannan na nufin shaidan zai kashe Almasihu, amma Allah zai tada shi da rai kuma, sa'annan Almasihu zai murkushe ikon shaidan har abada. Bayan shekaru da yawa, Allah ya bayyana cewa Yesu shine Almasihu.

Sa'anda Allah ya hallaka dukkan duniya da ruwan tsufana, ya yi tanadin jirgi domin ya ceci mutanen da suka bada gaskiya a gareshi. Hakannan kuma, kowa ya cancanci hallaka saboda zunubansa, amma Allah ya yi tanadin Yesu ya cece kowa dake bada gaskiya gareshi.

Darurruwan shekaru, Firistoci suna ci gaba da mika hadayu ga Allah saboda mutane domin su nuna irin hukuncin da ya cancanci zunubansu. Amma wadannan hadayu basu iya kawar da zunubansu ba. Yesu shine Babban Firist Mafi Girma. Ba kamar sauran firistoci ba, ya mika kansa a matsayin muhimmin hadaya da zai kawar da zunubi na dukkan mutanen duniya. Yesu shine cikakken Babban Firist saboda ya dauki hukunci na kowane zunubi da kowa ya taba aikatawa.

Allah yace wa Ibrahim, "Dukkan kabilu na mutanen duniya zasu sami albarka ta wurin ka." Yesu zuriyan Ibrahim ne. Dukkan kabilu na mutane sun sami albarka ta wurinsa, saboda duk wanda ya gaskanta da Yesu ya sami ceto daga zunubi, ya kuma zama zuriyar Ibrahim ta ruhaniya.

Sa'anda Allah yace wa Ibrahim ya mika dansa, Ishaku, a matsayin hadaya, Allah ya tanada rago domin hadayar amaimakon dansa, Ishaku. Dukkan mu mun cancanci mutuwa domin zunubanmu! Amma Allah ya tanada Yesu, 'Dan Ragon Allah, a matsayin hadaya, don ya mutu a madadinmu.

Sa'anda Allah ya aiko da annoba ta karshe a Masar, yace wa kowane iyalin Isra'ila su yanka rago marar aibi su watsa jinin a sama da gefen kofofinsu. Sa'anda Allah ya ga jinin, ya ketare gidajensu kuma bai kashe yayan farin su ba. Wannan alamari ana kiransa Ketarewa.

Yesu shine 'Dan Rago Ketarewar mu. Shi cikakke ne kuma marar zunubi, aka kuma kashe shi a lokacin idin Ketarewa. Sa'adda duk wani mutum ya gaskanta da Yesu, jinin Yesu ya biya hakin zunubin mutumin, kuma hukucin Allah ya ketare wannan mutum.

Allah ya yi alkawari da Isra'ilawa, wadanda sune zababbun mutanensa. Amma yanzu Allah ya yi sabon alkawari dake iya samuwa ga kowa. Saboda wannan sabon alkawari, kowane mutum daga kowane kabilun mutane zai iya zama daga cikin mutanen Allah ta wurin bada gaskiya ga Yesu.

Musa babban annabi ne wanda yayi shelar maganar Allah. Amma Yesu ne mafificin annabi na dukka. Shi Allah ne, saboda dukkan abinda ya yi ko ya fada, ayyukane da kuma kalmomin Allah. Don hakka aka ce da Yesu Kalmar Allah.

Allah yayi wa Sarki Dauda alkawari cewa daya daga zuriyar sa zai yi mulki a akan mutanen Allah a matsayin sarki har abada. Saboda Yesu Dan Allah ne kuma Almasihu, shine wannan kebabben zuriyar Dauda wanda zai iya mulki har abada.

Dauda sarkin Isra'ila ne, amma Yesu sarki ne na duniya gabaki daya! Zai sake dawowa yayi mulki da adalci da kuma salama, har abada.

Related information

Words of Life - Audio gospel messages in thousands of languages containing Bible based messages about salvation and Christian living.

Free downloads - Here you can find all the main GRN message scripts in several languages, plus pictures and other related materials, available for download.

The GRN Audio Library - Evangelistic and basic Bible teaching material appropriate to the people's need and culture in a variety of styles and formats.

Choosing the audio or video format to download - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons