unfoldingWord 48 - Yesu Shine Almasihun da aka yi Alkawarinsa

unfoldingWord 48 - Yesu Shine Almasihun da aka yi Alkawarinsa

Esquema: Genesis 1-3, 6, 14, 22; Exodus 12, 20; 2 Samuel 7; Hebrews 3:1-6, 4:14-5:10, 7:1-8:13, 9:11-10:18; Revelation 21

Número de guión: 1248

Idioma: Hausa

Audiencia: General

Tipo: Bible Stories & Teac

Propósito: Evangelism; Teaching

Citación Biblica: Paraphrase

Estado: Approved

Los guiones son pautas básicas para la traducción y grabación a otros idiomas. Deben adaptarse según sea necesario para que sean comprendidas y relevantes para cada cultura e idioma diferentes. Algunos términos y conceptos utilizados pueden necesitar más explicación o incluso ser reemplazados o omitidos por completo.

Guión de texto

Sa'anda Allah ya hallici duniya, kome na da kyau. Babu zunubi. Adamu da Hauwa'u na kaunar juna, kuma suna kaunar Allah. Babu cuta ko mutuwa. Hakkan nan Allah yake so duniya ta kasance.

Shaitan yayi magana tawurin macijin acikin gonar domin ya rudi Hauwa'u. Sai ita da Adamu suka yi wa Allah zunubi. Domin sun yi zunubi, kowa aduniya yana rashin lafiya kuma kowa na mutuwa.

Saboda Adamu da Hauwa'u sun yi zunubi, wani abin da ya fi wannan muni ya faru. Suka zama makiyan Allah. Sakamakon haka, tun daga lokacin nan kowane mutum an haife shi da dabi'ar zunubi kuma ya zama makiyin Allah. Dangantaka tsakanin Allah da mutane ta yanke saboda zunubi. Amma Allah yana da shirin maido da wannan dangantakar.

Allah yayi alkawari cewa daya daga cikin zuriyar Hauwa'u zai murkushe kan shaidan, shaidan kuwa zai yi wa diddigen sa rauni. Wannan na nufin shaidan zai kashe Almasihu, amma Allah zai tada shi da rai kuma, sa'annan Almasihu zai murkushe ikon shaidan har abada. Bayan shekaru da yawa, Allah ya bayyana cewa Yesu shine Almasihu.

Sa'anda Allah ya hallaka dukkan duniya da ruwan tsufana, ya yi tanadin jirgi domin ya ceci mutanen da suka bada gaskiya a gareshi. Hakannan kuma, kowa ya cancanci hallaka saboda zunubansa, amma Allah ya yi tanadin Yesu ya cece kowa dake bada gaskiya gareshi.

Darurruwan shekaru, Firistoci suna ci gaba da mika hadayu ga Allah saboda mutane domin su nuna irin hukuncin da ya cancanci zunubansu. Amma wadannan hadayu basu iya kawar da zunubansu ba. Yesu shine Babban Firist Mafi Girma. Ba kamar sauran firistoci ba, ya mika kansa a matsayin muhimmin hadaya da zai kawar da zunubi na dukkan mutanen duniya. Yesu shine cikakken Babban Firist saboda ya dauki hukunci na kowane zunubi da kowa ya taba aikatawa.

Allah yace wa Ibrahim, "Dukkan kabilu na mutanen duniya zasu sami albarka ta wurin ka." Yesu zuriyan Ibrahim ne. Dukkan kabilu na mutane sun sami albarka ta wurinsa, saboda duk wanda ya gaskanta da Yesu ya sami ceto daga zunubi, ya kuma zama zuriyar Ibrahim ta ruhaniya.

Sa'anda Allah yace wa Ibrahim ya mika dansa, Ishaku, a matsayin hadaya, Allah ya tanada rago domin hadayar amaimakon dansa, Ishaku. Dukkan mu mun cancanci mutuwa domin zunubanmu! Amma Allah ya tanada Yesu, 'Dan Ragon Allah, a matsayin hadaya, don ya mutu a madadinmu.

Sa'anda Allah ya aiko da annoba ta karshe a Masar, yace wa kowane iyalin Isra'ila su yanka rago marar aibi su watsa jinin a sama da gefen kofofinsu. Sa'anda Allah ya ga jinin, ya ketare gidajensu kuma bai kashe yayan farin su ba. Wannan alamari ana kiransa Ketarewa.

Yesu shine 'Dan Rago Ketarewar mu. Shi cikakke ne kuma marar zunubi, aka kuma kashe shi a lokacin idin Ketarewa. Sa'adda duk wani mutum ya gaskanta da Yesu, jinin Yesu ya biya hakin zunubin mutumin, kuma hukucin Allah ya ketare wannan mutum.

Allah ya yi alkawari da Isra'ilawa, wadanda sune zababbun mutanensa. Amma yanzu Allah ya yi sabon alkawari dake iya samuwa ga kowa. Saboda wannan sabon alkawari, kowane mutum daga kowane kabilun mutane zai iya zama daga cikin mutanen Allah ta wurin bada gaskiya ga Yesu.

Musa babban annabi ne wanda yayi shelar maganar Allah. Amma Yesu ne mafificin annabi na dukka. Shi Allah ne, saboda dukkan abinda ya yi ko ya fada, ayyukane da kuma kalmomin Allah. Don hakka aka ce da Yesu Kalmar Allah.

Allah yayi wa Sarki Dauda alkawari cewa daya daga zuriyar sa zai yi mulki a akan mutanen Allah a matsayin sarki har abada. Saboda Yesu Dan Allah ne kuma Almasihu, shine wannan kebabben zuriyar Dauda wanda zai iya mulki har abada.

Dauda sarkin Isra'ila ne, amma Yesu sarki ne na duniya gabaki daya! Zai sake dawowa yayi mulki da adalci da kuma salama, har abada.

Información relacionada

Palabras de Vida - GRN tiene mensajes audios en miles de idiomas que contienen mensajes basados en la Biblia acerca de la salvación y la vida cristiana.

Descargas gratis - Aquí puede encontrar los guiones principales de GRN en varios idiomas y también imágenes y otros materiales relacionados. Todos están disponibles para descargar.

Librería de audio de GRN - Material evangelistico y de enseñanza adecuado a las necesidades y a la cultura en variedad de stilos y formatos

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons

Choosing the right audio or video format - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?