unfoldingWord 28 - Saurayi Shugaba Mai arziki

unfoldingWord 28 - Saurayi Shugaba Mai arziki

Esquema: Matthew 19:16-30; Mark 10:17-31; Luke 18:18-30

Número de guión: 1228

Idioma: Hausa

Audiencia: General

Tipo: Bible Stories & Teac

Propósito: Evangelism; Teaching

Citación Biblica: Paraphrase

Estado: Approved

Los guiones son pautas básicas para la traducción y grabación a otros idiomas. Deben adaptarse según sea necesario para que sean comprendidas y relevantes para cada cultura e idioma diferentes. Algunos términos y conceptos utilizados pueden necesitar más explicación o incluso ser reemplazados o omitidos por completo.

Guión de texto

Wata rana, wani saurayi mai arziki shugaba ya zo wurin Yesu, ya yi masa tambaya, "Malam Managarci me zan yi domin in sami rai madawwami?'' Yesu ya ce masa, ''Don me ka kira ni 'managarci'? Managarci daya ne, shine Allah. Amma Idan kana so ka sami rai madawwami, kayi biyayya da dokokin Allah.''

Yayi tambaya, ''Wadanne ne nake bukata in yi biyayya da su?'' Yesu ya amsa, ''Kada ka yi kissan kai. Kada ka yi zina. Kada ka yi sata. Kada ka yi karya. Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, sannan ka kaunaci makwabcin ka kamar yadda ka ke kaunar kanka.''

Amma saurayin ya ce, ''Na yi biyayya da dukkan wadannan dokokin tun ina dan yaro. Me nake bukata kuma in yi domin in rayu har'abada?'' Yesu ya kalle shi ya kaunace shi.

Yesu ya amsa, ''Idan kana so ka zama cikakke, to, ka je ka sayar da dukkan mallakar ka, ka ba wa talakawa kudin, za ka sami dukiya a sama. Sa'annan ka zo ka bi ni.''

Da saurayin ya ji abin da Yesu ya fada, sai ya cika da bakin ciki, domin shi mai arziki ne sosai, kuma bai so ya ba da dukkan mallakarsa ba. Sai ya juya ya tafi daga wurin Yesu.

Sai Yesu ya ce wa almajiransa, "Yana da wuya kwarai ga mutane masu arziki su shiga mulkin Allah! I, ya fiye sauki rakumi ya shiga ta ramin allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.''

Sa'anda almajiran suka ji abin da Yesu ya fada, sai suka yi mamaki suka ce, "To wanene zai sami ceto?''

Yesu ya dubi almajiran , ya ce, ''Ga mutane wannan ba shi yiwuwa, amma da Allah kome mai yiwuwa ne.''

Bitrus ya ce wa Yesu, ''Mun bar kome mun bi ka, me zai zama sakamakon mu?''

Yesu ya amsa, ''Duk wanda ya bar gidaje, 'yan'uwa maza, da mata, uba da uwa, da 'ya'ya ko mallaka saboda ni, zai sami sama da ribi 100, ya kuma sami rai madawwami. Amma dayawa dake na farko za su zama na karshe, kuma wadanda ke na karshe za su zama na farko.''

Información relacionada

Palabras de Vida - GRN tiene mensajes audios en miles de idiomas que contienen mensajes basados en la Biblia acerca de la salvación y la vida cristiana.

Descargas gratis - Aquí puede encontrar los guiones principales de GRN en varios idiomas y también imágenes y otros materiales relacionados. Todos están disponibles para descargar.

Librería de audio de GRN - Material evangelistico y de enseñanza adecuado a las necesidades y a la cultura en variedad de stilos y formatos

Choosing the audio or video format to download - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons