unfoldingWord 02 - Zunubi Ya Shiga Duniya

unfoldingWord 02 - Zunubi Ya Shiga Duniya

Outline: Genesis 3

Script Number: 1202

Language: Hausa

Theme: Sin and Satan (Sin, disobedience, Punishment for guilt)

Audience: General

Genre: Bible Stories & Teac

Purpose: Evangelism; Teaching

Bible Quotation: Paraphrase

Status: Approved

Scripts are basic guidelines for translation and recording into other languages. They should be adapted as necessary to make them understandable and relevant for each different culture and language. Some terms and concepts used may need more explanation or even be replaced or omitted completely.

Script Text

Adamu da matarsa kuwa suna rayuwa cikin farin ciki, a kyakkyawar gonar da Allah ya yi masu. Babu wanda ke sanye da tufafi a cikin su, amma duk da haka basu ji kunya ba domin babu zunubi a duniya. Sau dayawa sukan yi tafiya tare da Allah suna kuma magana da shi.

Amma akwai wani mayaudarin maciji cikin gonar. Ya tambayi matar, ''Ko da gaske ne Allah ya gaya maku kada ku ci, 'ya'yan wani itace daga itatuwan da ke gonar?''

Sai matar ta amsa, "Allah ya ce mana zamu iya cin ya'yan kowanne itace amma banda na itacen sanin nagarta da mugunta. Allah ya fada mana, 'Idan kuka ci 'ya'yan itacen, ko kuka taba shi, zaku mutu."'

Macijin ya amsa wa matar, "Wannan ba gaskiya ba ne! Ba zaku mutu ba. Allah dai ya san cewa da zarar kun ci ya'yan itacen, zaku zama kamar Allah zaku kuma san nagarta da mugunta kamar yadda ya sani.''

Matar ta ga 'ya'yan itacen na da kyau da kuma bansha'awa. Tana kuma so ta zama mai hikima, sai ta tsinki wassu 'ya'yan itacen ta ci. Sai ta ba wa mijinta, wanda ke tare da ita, shi ma ya ci.

Nan take sai idanun su suka bude, suka gane tsirara suke. Suka yi kokarin rufe jikunan su, ta wurin dinka ganyaye domin suyi tufafi.

Sa'annan mutumin da matarsa suka ji motsin Allah yana tafiya a gonar. Sai dukkan su suka boye wa Allah. Sai Allah ya kira mutumin, "Ina kake?'' Adamu ya amsa, "Na ji tafiyarka a cikin gonar, na tsorata, domin tsirara na ke. Don haka na buya."

Sai Allah ya tambaye shi, "Wa ya gaya maka tsirara kake? Ko ka ci ya'yan itacen da na gaya maka kada ka ci?" Mutumin ya amsa, "Kai ka ba ni wannan mace, ita kuma ta ba ni 'ya'yan itacen." Allah kuma ya tambayi macen, "Me kenan ki ka yi?" Macen ta amsa, "Maciji ya yaudare ni."

Allah ya ce wa macijin, "An la'anta ka! Za ka yi tafiya rub da ciki, ka kuma ci kasa. Kai da macen za ku ki juna, sa'annan 'ya'yanka da ya'yanta zasu ki juna. Zuriyar macen zasu kuje kanka, kai kuma za ka yi wa diddigen sa rauni.

Allah kuma ya ce wa macen, "Zan sa haihuwa ta zama da zafi agareki. Muradin ki zai zama ga mijinki, shi kuma zai mallake ki.''

Allah ya ce wa mutumin, "Ka saurari matarka ka kuma yi mani rashin biyayya.Yanzu, an la'anta kasa, za ka kuma yi aiki tukuru, domin ka noma abinci. Sa'anan za ka mutu, jikin ka kuma zai koma turbaya.'' Mutumin ya kira matarsa Hawa'u, ma'ana, "mai bada rai," domin za ta zama uwa ga dukkan mutane. Sai Allah ya suturta Adamu da Hawa'u da fatun dabba.

Sai Allah yace, "Yanzu da 'yan Adam sun zama kamar mu, ta wurin sanin nagarta da mugunta, ba za'a yarda su ci 'ya'yan itacen rai su rayu har abada ba.'' Sai Allah ya kori Adamu da Hawa'u daga kyakyawar gonar. Allah ya sa mala'iku masu karfi a kofar gonar domin su hana duk wanda zai ci daga 'ya'yan itacen rai.

Related information

Words of Life - Audio gospel messages in thousands of languages containing Bible based messages about salvation and Christian living.

Free downloads - Here you can find all the main GRN message scripts in several languages, plus pictures and other related materials, available for download.

The GRN Audio Library - Evangelistic and basic Bible teaching material appropriate to the people's need and culture in a variety of styles and formats.

Choosing the audio or video format to download - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons