unfoldingWord 38 - An Bashe da Yesu

unfoldingWord 38 - An Bashe da Yesu

Outline: Matthew 26:14-56; Mark 14:10-50; Luke 22:1-53; John 18:1-11

Script Number: 1238

Language: Hausa

Audience: General

Genre: Bible Stories & Teac

Purpose: Evangelism; Teaching

Bible Quotation: Paraphrase

Status: Approved

Scripts are basic guidelines for translation and recording into other languages. They should be adapted as necessary to make them understandable and relevant for each different culture and language. Some terms and concepts used may need more explanation or even be replaced or omitted completely.

Script Text

Kowace shekara, Yahudawa su na bukin idin ketarewa. Wannan buki ne na yadda Allah ya ceci kakaninsu daga bauta a Masar shekaru masu yawa. Wajen shekaru uku bayan Yesu ya fara wa'azi da koyarwa afili, Yesu ya gaya wa almajiransa cewa ya na so ya yi bikin idin ketarewa da su a Urushalima, za a kuma kashe shi a can.

Daya daga cikin almajiran Yesu wani mutum ne mai suna Yahuza. Yahuza shine mai ajiye jakar kudin Manzanin, amma yana kaunar kudi, wassu lokatai ya kan saci kudi daga jakar. Bayan Yesu da almajiransa suka iso Urushalima, Yahuza ya je wajen shugabanin Yahudawa domin ya bashe da Yesu agare su a maimakon kudi. Ya san cewa shugabanin Yahudawan sun musanci Yesu shine Almasihu kuma suna shawara yadda zasu kashe shi.

Babban firist ya jagoranci, Shugabanin Yahudawan, suka biya Yahuza tsabar azurfa talatin domin ya bashe da Yesu. Wannan ya faru daidai yadda annabawa suka yi anabci. Yahuza ya yarda, ya karbi kudin, ya yi tafiyarsa. Ya fara neman zarafia yadda zai taimake su su kama Yesu.

A Urushalima, Yesu ya yi bikin idin ketarewa da almajiransa. A lokacin abinci idin, Yesu ya dauki gurasa ya gusura shi. Ya ce, "Karba ku ci wannan. Wannan jiki na ne, wanda aka bayar domin ku. Ku yi wannan domin ku tuna da ni." Ta wannan hanya, Yesu yace jikinsa zai zama hadaya domin su.

Sa'annan Yesu ya dauki koko yace, "Sha wannan. Jini na ne na sabon alkawari da aka zubar domin gafarar zunubai. Ku yi wannan don ku tuna da ni a kowane lokaci da ku ke shan sa.

Sai Yesu ya ce wa almajiransa, "Daya daga cikin ku zai bashe ni." Almajiran suka yi mamaki, sai suka tambaya, wa zai yi irin wannan abu. Yesu yace, "Mutumin da na bashi wannan gutsiren gurasa, shi ne mai bashewa." Sa'annan ya ba wa Yahuza gurasar.

Bayan da Yahuza ya karbi gurasar, Shaidan ya shige shi. Yahuza ya tafi don ya taimaki shugabannin Yahudawan kama Yesu. Da dare ne lokacin.

Bayan abincin, Yesu da almajiransa suka taka zuwa Dutsen Zaitun. Yesu yace, "Dukan ku za ku yashe ni cikin daren nan. A rubuce ya ke, 'Zan bugi makiyayin kuma dukkan tumakin za su watse.'"

Bitrus ya amsa, "Ko da sauran su dukka sun yashe ka, ni ba zan yashe ka ba!" Sai Yesu yace wa Bitrus, ''Shaidan yana so ya rinjaye dukkan ku, amma na yi maku addu'a Bitrus, cewa kada bangaskiyar ku ta kasa. Ko da haka ma, da daren nan, kafin zakara ya yi chara, za ka yi musun sani na sau uku cewa baka ma sanni ba."

Sai Bitrus ya ce wa Yesu, "Ko da ya zama dole in mutu, ba zan yi musun ka ba!" Sai duk sauran almajiran su ma suka ce haka.

Sa'annan Yesu ya tafi da almajiransa zuwa wani wuri da a ke ce da shi Getsemani. Yesu ya gaya wa almajiransa su yi addu'a domin kada su shiga cikin jaraba. Sa'annan Yesu ya tafi domin ya yi addu'a a kadaice.

Yesu ya yi addu'a sau uku, "Uba, idan zai yiwu, bari kada in sha wannan kokon wahala. Amma idan babu wata hanya da mutane za su sami gafarar zunubai, to bari nufin ka ya tabbata." Yesu ya damu kwarai sai zufar sa ta fara diga kamar jini. Allah ya aiko malai'ika ya karfafa shi.

Bayan kowane lokacin addu'a, Yesu dawo wurin almajiransa, amma suna barci. Sa'anda ya dawo karo na uku, Yesu yace, "Ku tashi! Mai bashe ni ya iso."

Yahuza ya zo da shugabanin Yahudawa, sojoji, da taron jama'a. Suna dauke da takuba da sanduna. Yahuza ya zo wurin Yesu yace, "Gaisuwa, Mallam," ya sumbace shi. Wannan shine alama ga shugabanin Yahudawa domin su san wanda zasu kama. Sai Yesu yace, "Yahuza, ka na bashe ni da sumba?"

Da sojojin suka kama Yesu, Bitrus ya zare takobinsa ya yanke kunnen wani baran babban firist. Yesu yace, "Mayar da takobin ka! Zan iya rokon Uba ya aiko da rundunar malai'iku su kare ni. Amma dole ne in yi biyayya da Ubana." Sa'annan Yesu ya warkar da kunnen mutumin. Bayan da aka kama Yesu, dukkan almajiran suka gudu.

Related information

Words of Life - Audio gospel messages in thousands of languages containing Bible based messages about salvation and Christian living.

Free downloads - Here you can find all the main GRN message scripts in several languages, plus pictures and other related materials, available for download.

The GRN Audio Library - Evangelistic and basic Bible teaching material appropriate to the people's need and culture in a variety of styles and formats.

Choosing the audio or video format to download - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons