unfoldingWord 40 - An Gicciye Yesu

unfoldingWord 40 - An Gicciye Yesu

Outline: Matthew 27:27-61; Mark 15:16-47; Luke 23:26-56; John 19:17-42

Script Number: 1240

Language: Hausa

Audience: General

Genre: Bible Stories & Teac

Purpose: Evangelism; Teaching

Bible Quotation: Paraphrase

Status: Approved

Scripts are basic guidelines for translation and recording into other languages. They should be adapted as necessary to make them understandable and relevant for each different culture and language. Some terms and concepts used may need more explanation or even be replaced or omitted completely.

Script Text

Bayan sojojin sun yi wa Yesu ba'a, sai suka tafi da shi domin su gicciye shi. Suka sa shi ya dauki gicciyen da zai mutu akai.

Sojojin suka kawo Yesu wurin da ake kira, "Kokon kai" suka kafe hannayensa da kafafunsa da kusa akan gicciye. Amma Yesu ya ce, "Uba ka gafarta masu domin basu san abin da suke yi ba." Bilatus ya bada umarni su rubuta, "Sarkin Yahudawa" akan allo su kuma sa shi akan gicciyen, sama da kan Yesu.

Sojojin suka yi kuri'a akan tufafin Yesu. Sa'anda suka yi haka, sun cika wani annabci da ya ce, "Sun raba tufafina a tsakaninsu, suka sa kuri'a akan tufa ta."

Aka gicciye Yesu tsakanin 'yan fashi biyu. Daya daga cikinsu ya yi wa Yesu ba'a, amma dayan ya ce, "Baka da tsoron Allah? mu mun yi laifi amma wannan mutumin bashi da laifi." Sa'anan ya ce wa Yesu, "In ka yarda ka tuna da ni a mulkinka." Yesu ya amsa masa. "Yau zaka kasance tare da ni a fiddausi."

Shugbannin Yahudawa da wadansu mutane a cikin taron suka yi wa Yesu ba'a. Suka ce masa, "Idan kai 'Dan Allah ne sauko daga kan gicciyen ka ceci kanka! sa'annan zamu gaskanta ka."

Sai sararin sama na lardin ya yi baki gaba daya, ko da yake da tsakiyar rana ne. Wuri ya zama duhu da tsakar rana, aka kuma ci gaba da duhu har sa'a uku.

Sa'anan Yesu yi kuka, "Ya kare! Uba na bada ruhu na a cikin hannun ka." Sai ya sunkuyar da kansa ya saki ruhunsa. Da ya mutu an yi girgizar kasa, sai babban labulen da ya raba mutane da Allah a Haikali, ya tsage biyu, daga sama zuwa kasa.

Ta wurin mutuwarsa, Yesu ya bude hanya da mutane za su zo gun Allah. Da sojan nan mai tsaron Yesu ya ga dukkan abubuwan da suka faru, sai ya ce, "Hakika, wannan mutumin marar laifi ne. Shi Dan Allah ne."

Sa'annan Yusufu da NIkodimas, shugabannin Yahudawa biyu wadanda suka gaskanta, Yesu Almasihu ne, suka tambayi Bilatus jikin Yesu. Suka nade jikinsa cikin zani suka sa shi cikin kabarin dutse da aka sassaka. Sa'anan suka mirgina babban dutse a bakin kabarin domin su rufe kofar.

Related information

Words of Life - Audio gospel messages in thousands of languages containing Bible based messages about salvation and Christian living.

Free downloads - Here you can find all the main GRN message scripts in several languages, plus pictures and other related materials, available for download.

The GRN Audio Library - Evangelistic and basic Bible teaching material appropriate to the people's need and culture in a variety of styles and formats.

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons

Choosing the right audio or video format - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?