unfoldingWord 24 - Yahaya ya yi wa Yesu Baftisma

unfoldingWord 24 - Yahaya ya yi wa Yesu Baftisma

Raamwerk: Matthew 3; Mark 1; Luke 3; John 1:15-37

Skripnommer: 1224

Taal: Hausa

Gehoor: General

Genre: Bible Stories & Teac

Doel: Evangelism; Teaching

Bybelaanhaling: Paraphrase

Status: Approved

Skrips is basiese riglyne vir vertaling en opname in ander tale. Hulle moet so nodig aangepas word dat hulle verstaanbaar en relevant is vir elke verskillende kultuur en taal. Sommige terme en konsepte wat gebruik word, het moontlik meer verduideliking nodig of selfs heeltemal vervang of weggelaat word.

Skripteks

Yahaya, 'dan Zakariya da Alisabatu, ya yi girma ya kuma zama annabi. Yayi rayuwa cikin jeji, yana cin zuma da fara, ya na kuma sanye da tufafin da aka yi da gashin rakumi.

Mutane da dama suka fito zuwa jejin domin su saurari Yahaya. Sai ya yi masu wa'azi, ya na cewa, "Ku tuba domin mulkin Allah ya kusa!"

Da mutane suka ji sakon Yahana, da yawa daga cikinsu suka tuba daga zunubansu, sai Yahaya ya yi masu baftisma. Shugabanin addini da yawa suka zo wurin Yahaya domin ya yi masu baftisma, amma basu tuba ko kuma su furta zunubansu ba.

Yahaya ya ce wa shugabanin addinin, "Ku macizai masu dafi! Ku tuba ku sake halayen ku. Duk itacen da bata bada 'ya'ya mai kyau ba, za a sare ta a jefa ta cikin wuta." Yahaya ya cika abin da annabawa suka fada, "Duba, na aiko manzo na, a yariga ka gaba, wanda zai shirya hanyar ka."

Wassu daga cikin Yahudawan suka tambayi Yahaya ko shi ne Almasihu, Yahaya kuwa ya amsa, "Bani ne Almasihun ba, amma akwai wanda ke biye da ni. Shi mai girma ne, wanda ban isa in kwance takalmansa ba.''

Kashe gari, Sai Yesu yazo domin Yahaya ya yi masa baftisma. Da Yahaya ya ganshi, sai ya ce, "Duba! Ga 'Dan Rago na Allah wanda zai kawar da zunuban duniya."

Yahaya ya ce wa Yesu, "Ban isa in yi maka baftisma ba. Maimakon haka kaine zaka yi mani baftisma.'' Amma Yesu yace, ''Kayi mani baftisma, domin abin da ya dace ne ayi." Hakanan Yahaya ya yi masa baftisma, ko da shike Yesu bai taba yin zunubi ba.

Sa'anda Yesu ya fito daga ruwa, bayan an yi masa baftisma, sai Ruhun Allah ya bayyana a misalin kurciya ya sauko a kansa. A wannan lokaci, muryar Allah yayi magana daga sama, yana cewa, "Kai 'Da na ne wanda nake kauna, ina kuma farin ciki da kai sosai."

Allah ya fadawa Yahaya, "Ruhu Mai Tsarki zai sauko kan wani wanda zaka yi masa baftisma. Wannan mutumin shi ne 'Dan Allah." Allah daya ne. Amma da Yahaya ya yi wa Yesu baftisma, ya ji Allah Uba yayi magana, ya ga Allah 'Da, shi ne Yesu, ya kuma ga Ruhu Mai Tsarki.

Verwante inligting

Woorde van Lewe - GRN het oudio-evangelieboodskappe in duisende tale wat Bybelgebaseerde boodskappe bevat oor verlossing en Christelike lewe.

Gratis aflaaie - Hier vind u al die belangrikste GRN boodskap skrips in verskeie tale, plus prente en ander verwante materiaal, wat beskikbaar is om af te laai.

Die GRN Oudiobiblioteek - Evangelistiese en basiese Bybelonderrigmateriaal wat geskik is vir die behoefte en kultuur van die mense in 'n verskeidenheid style en formate.

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons

Choosing the right audio or video format - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?