Khetha Ulimi

mic

unfoldingWord 10 - Annoba goma

unfoldingWord 10 - Annoba goma

Uhlaka: Exodus 5-10

Inombolo Yeskripthi: 1210

Ulimi: Hausa

Izilaleli: General

Inhloso: Evangelism; Teaching

Features: Bible Stories; Paraphrase Scripture

Isimo: Approved

Imibhalo ayiziqondiso eziyisisekelo zokuhunyushwa nokuqoshwa kwezinye izilimi. Kufanele zishintshwe njengoba kunesidingo ukuze ziqondakale futhi zihambisane nesiko nolimi oluhlukene. Amanye amagama nemiqondo esetshenzisiwe ingase idinge incazelo eyengeziwe noma ishintshwe noma ikhishwe ngokuphelele.

Umbhalo Weskripthi

Musa da Haruna sun je wurin Fir'auna. Suka ce, "Ga abinda Allah na Isra'ila ya ce, saki mutane na su tafi!" Fir'auna bai saurare su ba maimakon ya saki 'yayan Isra'ila su tafi, sai ya tilasta su suyi aiki mafi tsanani!

Fir'auna yayi ta kin barin mutanen su tafi, Sai Allah ya aiko da munana annoba guda goma a kan Masar. Ta wurin wandanan annoba, Allah ya nuna wa Fir'auna da allolin masar cewa ya fi su iko.

Allah ya mayar da kogin Nilo jini, Duk da haka Fir'auna bai saki Isra'ilawa su tafi ba.

Allah ya aiko da kwadi a dukan Masar. Fir'auna ya roki Musa ya kawar da kwadin. Amma bayan da duka kwadin sun mutu, Fir'auna ya taurare zuciyarsa kuma ya ki ya saki Isra'ilawa su bar Masar.

Saboda haka Allah ya aiko da annobar kwarkwata. Bayan haka sai Allah ya aiko da annobar kuda. Fir'auna ya kira Musa da Haruna ya fada masu idan sun tsayar da annobar, Isra'ilawa za su iya barin Masar. Da Musa ya yi adu'a, Allah ya kawar da dukan kudan daga Masar. Amma Fir'auna ya taurara zuciyarsa ya ki ya saki mutane su tafi.

Bayan haka, Allah ya sa duka dabbobin da a ke kiwo a gonakin Masarawa su kamu da cuta su mutu. Amma Fir'auna ya taurara zuciyarsa bai saki Isra'ilawa su tafi ba.

Sai Allah ya fada wa Musa ya watsa toka a iska a gaban Fir'auna. Da ya yi haka, sai marurai masu zafi sun fita akan Masarawa, amma ba a kan Isra'ilawa ba. Allah ya taurara zuciyar Fir'auna, kuma bai saki Isra'ilawan su tafi ba.

Bayan haka, Allah ya aiko da kankara da ya lalatar da mafi yawan amfanin gona da ke Masar ya kuma kashe duk wanda ya je wuje. Fir'auna ya kira Musa da Haruna ya kuma fada masu, "Na yi zunubi. za ku iya tafiya." Sai Musa ya yi adu'a, sa'annan kankaran ya daina fadowa daga sama.

Amma Fir'auna ya sake yin zunubi, ya kuma taurara zuciyarsa, ya ki ya saki Isra'ilawa su tafi.

Saboda haka Allah ya aiko da tarin fari su zo kan Masar. Wadannan farin sun cinye dukan amfani da kankaran bai lalatar ba.

Sai Allah ya aiko da duhun da ya dauki sawon kwana uku. Duhun yayi sanani har Masarawan ba su iya barin gidajensu. Amma a kwai haske a inda Isra'ilawa suke zama.

Ko bayan annoban nan tara, har yanzu Fir'auna ya ki ya saki Isra'ilawa su tafi. Tunda Fir'auna ya ki ji, Allah ya yi niyar aiko da annoba daya na karshe. Wannan zai sauya tananin Fir'auna.

Ulwazi oluhlobene

Amazwi Okuphila - Imiyalezo yevangeli elalelwayo ngezinkulungwane zezilimi equkethe imiyalezo esekelwe eBhayibhelini mayelana nensindiso nokuphila kobuKristu.

Choosing the audio or video format to download - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?

Copyright and Licensing - GRN shares its audio, video and written scripts under Creative Commons