unfoldingWord 31 - Yesu ya yi Tafiya a kan Ruwa
Anahat: Matthew 14:22-33; Mark 6:45-52; John 6:16-21
Komut Dosyası Numarası: 1231
Dil: Hausa
Kitle: General
Amaç: Evangelism; Teaching
Features: Bible Stories; Paraphrase Scripture
Durum: Approved
Komut dosyaları, diğer dillere çeviri ve kayıt için temel yönergelerdir. Her bir farklı kültür ve dil için anlaşılır ve alakalı hale getirmek için gerektiği gibi uyarlanmalıdırlar. Kullanılan bazı terimler ve kavramlar daha fazla açıklamaya ihtiyaç duyabilir veya hatta tamamen değiştirilebilir veya atlanabilir.
Komut Dosyası Metni
Sa'annan Yesu ya fada wa almajiransa su shiga jirgin ruwa su haye zuwa wancan gefen tafki sa'adda da ya tsaya ya sallami taron. Bayan Yesu ya sallami taron, sai ya haura gefen tsauni domin ya yi addu'a. Yesu na wurin nan shi kadai, ya kuma yi addu'a har zuwa kurewar dare.
A wannan lokaci, almajiran na tukin jirgin ruwansu, amma a kurewar daren, sun kai tsakiyar ruwan ne kawai. Suna tuki da wahala, domin iska na hurawa da karfi gaba da su sosai.
Sa'annan Yesu ya gama addu'a sai ya tafi wurin almajiran. Yayi tafiya akan ruwa yana haye tafkin zuwa wurin jirgin su!
Almajiran suka tsorata kwarai da suka ga Yesu, domin a tunaninsu fatalwa suke gani. Yesu ya san cewa tasorace suke, sai ya kira su, ya ce, "Kada ku ji tsoro. Ni ne!"
Sai Bitrus ya ce wa Yesu, "Ya shugaba, idan dai kai ne, ka umarce ni in zo wurin ka a kan ruwan." Yesu ya ce wa Bitrus, "Zo!"
Sai Bitrus ya fita daga jirgin ruwar ya fara tafiya zuwa wurin Yesu a kan ruwa. Amma da yayi tafiya kadan, sai ya kau da idanunsa daga Yesu ya fara duban rakuman ruwa, yana jin yadda kakkarfar iskar take.
Sai Bitrus ya ji tsoro ya kuma fara nutsewa a ruwa. Sai yayi kuka, "Ya shugaba, ka cece ni!" Nandanan Yesu ya isa wurin sa ya kama shi. Sa'annan ya ce wa Bitrus, "Kai mutum mai karamin bangaskiya, me ya sa ka yi shakka?"
A lokacin da Bitrus da Yesu suka shiga jirgin ruwan, nan da nan iskar ta dena kadawa, ruwan kuma ya natsu. Almajiran suka yi mamaki. Suka yi wa Yesu sujada, suna cewa, "Gaskiya, kai Dan Allah ne."