unfoldingWord 35 - Labarin Uba Mai Tausayi
Obrys: Luke 15
Číslo skriptu: 1235
Jazyk: Hausa
publikum: General
Účel: Evangelism; Teaching
Features: Bible Stories; Paraphrase Scripture
Postavenie: Approved
Skripty sú základnými usmerneniami pre preklad a nahrávanie do iných jazykov. Mali by byť podľa potreby prispôsobené, aby boli zrozumiteľné a relevantné pre každú odlišnú kultúru a jazyk. Niektoré použité termíny a koncepty môžu vyžadovať podrobnejšie vysvetlenie alebo môžu byť dokonca nahradené alebo úplne vynechané.
Text skriptu
Wata rana, Yesu na koyar wa, masu karbar haraji masu yawa da wadansu masu zunubi suka taru domin su saurare shi.
Wadansu shugabannin addini dake wurin suka ga Yesu yana ma'amala da masu zunubi a matsayin abokai, sai suka fara zargin sa a tsakansu. Sai Yesu ya fada masu wannan labari.
"Akwai wani mutum wanda yake da 'ya'ya biyu. Karamin dan ya ce wa Ubansa, 'Baba, ina son rabon gado na yanzu!' Sai uban ya raba dukiyarsa tsakanin 'ya'yan guda biyu."
"Bada jimawa ba sai karamin dan ya tara dukkan abinda yake da shi ya tafi da nisa ya barnatar da kudin sa cikin rayuwar zunubi."
"Bayan haka, aka yi fari mai tsanani a kasar da karamin dan yake, kuma bashi da kudin sayan abinci. Sai ya karbi aiki da ya samu, na ciyad da aladu. Ya zamana da bakin ciki kuma ga yunwa har ma yana so ya ci abincin aladu."
"'A karshe, karamin dan yace wa kansa, 'Me nake yi? Dukkan barorin ubana suna da abinci da yawa, amma gani nan ina fama da yunwa. Zan koma gun ubana in roke shi in zama daya daga cikin barorin sa."'
"Sai karamin dan ya kama hanyar zuwa gidan uban sa. Tun yana nesa, uban ya hango shi ya ji tausayin sa. Ya ruga zuwa wurin dansa ya kuma rungume shi ya sumbace shi."
"Dan yace, 'Baba, na yi wa Allah zunubi na kuma yi maka. Ban cancanci in zama dan ka ba.'"
"Amma ubansa yace wa daya daga cikin barorinsa, 'Je ka da sauri ka kawo tufafi mafi kyau ka sa wa dana! Ka sa zobe a yatsarsa ka kuma sa takalma a kafafunsa. Sai ka yanka dan maraki mafi kyau, domin mu yi bukin farin ciki, domin dana ya mutu, amma yanzu ya rayu! Ya bata, amma yanzu an same shi!"'
"Sai mutanen suka fara bukki. Bada jimawa ba, sai ga babban dan ya dawo gida daga aiki a goma. Ya ji kide-kide da raye-raye, ya yi tunanin me ke faruwa."
"Sa'anda babban dan ya gane cewa ana bukki domin dan'uwansa ne ya komo gida, sai ya husata kuma yaki shiga gidan. Ubansa ya fito ya roke shi ya shigo yayi bukin dasu, amma ya ki."
"Sai babban dan yace wa ubansa, 'Dukkan shekarun nan nayi maka aiki da aminci! Ban taba yi maka rashin biyayya ba, duk da haka baka bani ko dan akuya in yi buki da abokaina ba. Amma sa'adda wannan dan naka wanda ya batar da kudinka cikin aikin zunubi ya komo gida, ka yanka dan maraki mafi kyau domin sa!'"
"Sai uban ya amsa, 'Dana, kana tare dani kullum, kuma dukkan abinda nake dashi naka ne. Amma daidai ne muyi buki, domin dan'uwanka ya mutu, amma yanzu yana raye. Ya bata, amma yanzu an same shi!'"