unfoldingWord 50 - Dawowar Yesu

unfoldingWord 50 - Dawowar Yesu

Esquema: Matthew 13:24-42; 22:13; 24:14; 28:18; John 4:35; 15:20; 16:33; 1 Thessalonians 4:13-5:11; James 1:12; Revelation 2:10; 20:10; 21-22

Número de guión: 1250

Idioma: Hausa

Audiencia: General

Tipo: Bible Stories & Teac

Propósito: Evangelism; Teaching

Citación Biblica: Paraphrase

Estado: Approved

Los guiones son pautas básicas para la traducción y grabación a otros idiomas. Deben adaptarse según sea necesario para que sean comprendidas y relevantes para cada cultura e idioma diferentes. Algunos términos y conceptos utilizados pueden necesitar más explicación o incluso ser reemplazados o omitidos por completo.

Guión de texto

Kusan shekaru 2000, kari bisa kari na mutane a duniya suna sauraron labari mai dadin nan game Yesu wanda Almasihun. Ikklisiya ta na ta girma. Yesu ya yi alkawari zai dawo a karshen duniya. Ko da yake bai dawo ba tukuna, zai cika alkawarinsa.

Yayin da muke jiran dawowar Yesu, Allah yana so muyi rayuwar a hanya ta tsarki da ke girmama shi. Yana kuma so mu fada wa wadansu game da mulkin sa. Lokacin da Yesu ke rayuwa a duniya, ya ce, "Almajiraina za su yi wa'azin labari mai dadin nan game da mulkin Allah ga mutane ko'ina a duniya, sa'annan karshe zai zo."

Kabilun mutane da yawa har yanzu basu ji labarin Yesu ba. Kafin tafiyar sa sama, Yesu ya fada wa Kiristoci su yi wa'azin labari mai dadin nan ga mutanen da ba su taba ji ba. Ya ce, "Ku je ku almajirantar da dukkan kabilun mutane!" kuma, "Filaye sun nuna domin girbi!"

Yesu ya kuma ce, "Bara dai, bai fi maigidansa girma ba. Kamar yadda hukumomin duniyan nan suka ki ni, za su azabtar da ku, su kuma kashe ku saboda ni. Ko da yake a wannan duniya za ku sha wahala, ku sami karfafawa domin Na yi nasara da Shaidan, wanda ke mulkin duniyan nan. Idan kuka ci gaba da aminci da ni har zuwa karshe, Allah zai cece ku!''

Yesu ya fada wa almajiransa wani labari wanda zai bayyana abin da zai faru da mutane a lokacin da duniya ta kai ga karshe. Ya ce, "Wani mutum ya shuka iri mai kyau a filinsa. Sa'anda ya ke barci, makiyin sa ya zo ya shuka wuta-wuta tare da alkamar, sai ya tafi abinsa."

"Sa'anda da shukan suka fito, barorin mutumin suka ce, 'Maigida, ka shuka iri mai kyau a filin can. Me ya sa akwai wuta-wuta a ciki?' Maigidan ya amsa, 'Wani makiyi ne lallai ya shuka su."'

'Barorin sun amsa wa maigidansu suka ce, 'Ko mu tuge wuta-wutan ne?' Maigidan ya ce, 'A'a. Idan kuka yi haka, za ku tuge wassu alkama tare da su. Ku dakata zuwa lokacin girbi sa'annan za ku tara wuta-wutan dami dami a kone su, amma ku kawo alkamar a cikin rumbu na.'

Almajiran ba su gane ma'anar labarin ba, sai suka roki Yesu ya bayyana masu. Yesu ya ce, "Mutumin da ya shuka iri mai kyau, yana a madadin Almasihu. Filin kuma, a madadin duniya. Iri mai kyau kuma, a madadin mutane na mulkin Allah."

"Wuta-wutan kuma, a madadin mutanen da ke na mugun. Makiyin nan da ya shuka wuta-wuta kuma, a madadin iblis. Girbin kuma, a madadin karshen duniya, masu yin girbin kuma, a madadin mala'ikun Allah."

"Lokacin da duniya ta zo karshe, mala'iku za su tattara dukan mutane da ke na iblis, su kuma jefa su cikin wuta mai ruruwa, inda za su yi kuka da cizon hakora a cikin azaba mai tsanani. Sa'annan adalai za su haskaka kamar rana cikin mulkin Allah Ubansu."

Yesu kuma ya ce zai dawo duniya, kafin duniyar ta zo ga karshe. Zai dawo kamar yadda ya tafi, wannan na nufin, zai kasance cikin jiki, zai zo bisa gajimare na sararin sama. Lokacin da Yesu zai dawo, duk Kiristan da ya mutu zai tashi daga matattu ya same shi a sararin sama.

Sa'annan Kiristocin da ke a raye har yanzu kuma za su tashi zuwa cikin sararin sama, su hadu da sauran Kiristoci da suka tashi daga matattu. A can, dukkansu za su kasance tare da Yesu. Bayan haka, Yesu zai zauna tare da mutanensa cikin cikakkiyar salama da dayantaka na har abada.

Yesu ya yi alkawari zai ba da rawani ga dukkan wadanda suka gaskanta da shi. Za su yi rayuwa, su kuma yi mulki tare da Allah cikin cikakkiyar salama na har abada.

Amma Allah zai shar'anta dukkan wanda bai bada gaskiya ga Yesu ba. Zai jefa su cikin jahannama, inda za su yi kuka da cizon hakora cikin kunci na har abada. Wutan da ba ta mutuwa, za ta ci gaba da kona su, tsutsotsi kuma ba za su daina cin su ba.

Lokacin da Yesu zai dawo, zai hallaka Shaidan gaba daya da mulkin sa. Zai jefa Shaidan cikin jahannama inda zai kone har abada, tare da duk wanda ya zaba ya bi shi, a maimakon yin biyayya ga Allah.

Domin Adamu da Hauwa'u sun yi wa Allah rashin biyayya, sun kuma kawo zunubi a wannan duniya, Allah ya la'anta ta, ya kuma yanke shawara ya hallaka ta. Amma wata rana, Allah zai hallici sabuwar sama da sabuwar duniya da za ta zama cikakkiya.

Yesu da mutanensa za su zauna a sabuwar duniyar, kuma zai yi mulki na har abada bisa dukkan kome da ya kasance. Zai share dukkan hawaye, kuma ba za a kara samun wahala, bakin ciki, kuka, mugunta, ciwo, ko mutuwa ba. Yesu zai yi sarautar mulkin sa da salama da adalci, zai kuma kasance tare da mutanensa har abada.

Información relacionada

Palabras de Vida - GRN tiene mensajes audios en miles de idiomas que contienen mensajes basados en la Biblia acerca de la salvación y la vida cristiana.

Descargas gratis - Aquí puede encontrar los guiones principales de GRN en varios idiomas y también imágenes y otros materiales relacionados. Todos están disponibles para descargar.

Librería de audio de GRN - Material evangelistico y de enseñanza adecuado a las necesidades y a la cultura en variedad de stilos y formatos

Choosing the audio or video format to download - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons