Επιλέξτε μια Γλώσσα

mic

unfoldingWord 28 - Saurayi Shugaba Mai arziki

unfoldingWord 28 - Saurayi Shugaba Mai arziki

Περίγραμμα: Matthew 19:16-30; Mark 10:17-31; Luke 18:18-30

Αριθμός σεναρίου: 1228

Γλώσσα: Hausa

Κοινό: General

Σκοπός: Evangelism; Teaching

Features: Bible Stories; Paraphrase Scripture

Κατάσταση: Approved

Τα σενάρια είναι βασικές οδηγίες για μετάφραση και ηχογράφηση σε άλλες γλώσσες. Θα πρέπει να προσαρμόζονται όπως είναι απαραίτητο για να είναι κατανοητές και σχετικές με κάθε διαφορετική κουλτούρα και γλώσσα. Ορισμένοι όροι και έννοιες που χρησιμοποιούνται μπορεί να χρειάζονται περισσότερη εξήγηση ή ακόμη και να αντικατασταθούν ή να παραλειφθούν εντελώς.

Κείμενο σεναρίου

Wata rana, wani saurayi mai arziki shugaba ya zo wurin Yesu, ya yi masa tambaya, "Malam Managarci me zan yi domin in sami rai madawwami?'' Yesu ya ce masa, ''Don me ka kira ni 'managarci'? Managarci daya ne, shine Allah. Amma Idan kana so ka sami rai madawwami, kayi biyayya da dokokin Allah.''

Yayi tambaya, ''Wadanne ne nake bukata in yi biyayya da su?'' Yesu ya amsa, ''Kada ka yi kissan kai. Kada ka yi zina. Kada ka yi sata. Kada ka yi karya. Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, sannan ka kaunaci makwabcin ka kamar yadda ka ke kaunar kanka.''

Amma saurayin ya ce, ''Na yi biyayya da dukkan wadannan dokokin tun ina dan yaro. Me nake bukata kuma in yi domin in rayu har'abada?'' Yesu ya kalle shi ya kaunace shi.

Yesu ya amsa, ''Idan kana so ka zama cikakke, to, ka je ka sayar da dukkan mallakar ka, ka ba wa talakawa kudin, za ka sami dukiya a sama. Sa'annan ka zo ka bi ni.''

Da saurayin ya ji abin da Yesu ya fada, sai ya cika da bakin ciki, domin shi mai arziki ne sosai, kuma bai so ya ba da dukkan mallakarsa ba. Sai ya juya ya tafi daga wurin Yesu.

Sai Yesu ya ce wa almajiransa, "Yana da wuya kwarai ga mutane masu arziki su shiga mulkin Allah! I, ya fiye sauki rakumi ya shiga ta ramin allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.''

Sa'anda almajiran suka ji abin da Yesu ya fada, sai suka yi mamaki suka ce, "To wanene zai sami ceto?''

Yesu ya dubi almajiran , ya ce, ''Ga mutane wannan ba shi yiwuwa, amma da Allah kome mai yiwuwa ne.''

Bitrus ya ce wa Yesu, ''Mun bar kome mun bi ka, me zai zama sakamakon mu?''

Yesu ya amsa, ''Duk wanda ya bar gidaje, 'yan'uwa maza, da mata, uba da uwa, da 'ya'ya ko mallaka saboda ni, zai sami sama da ribi 100, ya kuma sami rai madawwami. Amma dayawa dake na farko za su zama na karshe, kuma wadanda ke na karshe za su zama na farko.''

Σχετική πληροφορία

Λόγια Ζωής - Ηχητικά μηνύματα του ευαγγελίου σε χιλιάδες γλώσσες που περιέχουν μηνύματα βασισμένα στη Βίβλο για τη σωτηρία και τη χριστιανική ζωή.

Choosing the audio or video format to download - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?

Copyright and Licensing - GRN shares its audio, video and written scripts under Creative Commons