unfoldingWord 05 - Dan Alkawari

unfoldingWord 05 - Dan Alkawari

Outline: Genesis 16-22

Script Number: 1205

Language: Hausa

Audience: General

Genre: Bible Stories & Teac

Purpose: Evangelism; Teaching

Bible Quotation: Paraphrase

Status: Approved

Scripts are basic guidelines for translation and recording into other languages. They should be adapted as necessary to make them understandable and relevant for each different culture and language. Some terms and concepts used may need more explanation or even be replaced or omitted completely.

Script Text

Bayan shekaru goma da isowar Abram da Saraya cikin Kan'ana, har yanzu basu sami 'da ba. Sai matar Abram, Saraya, ta ce masa, "Tunda Allah bai yarda mini in sami yara ba gashi yanzu na tsufa na kure don haihuwan 'ya'ya, ga baranya ta Hajaratu. Ka aureta domin ta haifi mani da.''

Sai Abram ya auri Hajaratu. Hajaratu ta haifi da namiji, Abram kuma ya bashi suna Isma'ilu. Amma Saratu yi kishin Hajaratu. Da Isma'ilu ya kai shekara 13, Allah ya sake magana da Abram.

Allah ya ce, " Ni ne Allah Mai Iko dukka. Zan yi alkawari da kai." Sai Abram ya yi ruku'u har kasa. Allah kuma ya ce wa Abram, "Zaka zama uban kabilu da yawa. Zan baka da zuriyarka kasar Kan'ana abin gado, kuma zan zama Allahnsu har abada. Dole ka yi wa kowane da namiji a iyalinka kaciya.''

Matarka, Saraya, zata sami da-zai zama dan alkawari. Ka bashi suna Ishaku. Zan yi alkawarina da shi, zai kuma zama babbar kabila. Zan maida Isma'ilu babban kabila kuma, amma alkawarina da Ishaku ne. Sai Allah ya sauya sunan Abram zuwa Ibrahim, ma'ana, "Uban masu yawa." Allah kuma ya sauya sunan Saraya zuwa Saratu, ma'ana, "gimbiya."

A wannan ranar Ibrahim ya yi wa duk mazajen da ke gidansa kaciya. Bayan shekara guda, sa'adda Ibrahim ya kai shekaru 100, Saratu kuma ta yi 90, Saratu ta haifa wa Ibrahim da. Suka bashi suna Ishaku kamar yadda Allah ya gaya masu su yi.

Sa'anda Ishaku ya ke dan saurayi, Allah ya gwada bangaskiyar Ibrahim da cewa, "Dauki Ishaku tilon danka ka kashe shi, ya zama hadaya a gareni." Sai kuma Ibrahim ya yi biyayya da Allah, ya shirya ya yi hadaya da 'dansa.

Sa'anda Ibrahim da Ishaku suke tafiya wurin hadaya, Ishaku ya yi tambaya, "Baba, muna da itace domin hadaya, amma ina dan ragon?'' Ibrahim ya amsa, "Allah zai tanada ragon hadaya, 'dana."

Da suka isa wurin hadaya, Ibrahim ya daure dansa Ishaku, ya kwantar da shi akan bagadi. Zai kashe dansa kenan, sai Allah ya ce, ''Dakata! Kada ka yi wa yaron rauni! Yanzu na san kana tsorona, domin baka hana mani danka tilo ba."

A kusa da wurin Ibrahim ya ga rago a sarkafe cikin daji. Allah ya riga ya tanada ragon hadaya amaimakon Ishaku. Da farin ciki Ibrahim ya mika ragon hadaya.

Sa'annan Allah ya ce wa Ibrahim, "Saboda ka amince ka bani kome, harma danka tilo, Na yi alkawari in albarkace ka. Zuriyarka zata fi taurarin sama yawa. Domin ka yi mani biyayya, dukkan iyalan duniya za su zama da albarka ta wurin iyalinka.''

Related information

Words of Life - Audio gospel messages in thousands of languages containing Bible based messages about salvation and Christian living.

Free downloads - Here you can find all the main GRN message scripts in several languages, plus pictures and other related materials, available for download.

The GRN Audio Library - Evangelistic and basic Bible teaching material appropriate to the people's need and culture in a variety of styles and formats.

Choosing the audio or video format to download - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons