unfoldingWord 22 - Haihuwar Yahaya

unfoldingWord 22 - Haihuwar Yahaya

Zusammenfassung: Luke 1

Skript Nummer: 1222

Sprache: Hausa

Zuschauer: General

Genre: Bible Stories & Teac

Zweck: Evangelism; Teaching

Bibelzitat: Paraphrase

Status: Approved

Skripte dienen als grundlegende Richtlinie für die Übersetzung und Aufnahme in anderen Sprachen. Sie sollten, soweit erforderlich, angepasst werden, um sie für die jeweilige Kultur und Sprache verständlich und relevant zu machen. Einige der verwendeten Begriffe und Konzepte müssen unter Umständen ausführlicher erklärt oder sogar ersetzt oder ganz entfernt werden.

Skript Text

A zamanin da, Allah yayi magana da mutanensa ta wurin mala'iku da annabawa. Amma shekaru 400 suka wuce da bai yi masu magana ba. Ba labari sai wani mala'ika ya zo da sako daga Allah zuwa warin tsohon firist mai suna Zakariya. Zakariya da matarsa, Alisabatu, mutane masu tsoron Allah ne, amma ba ta iya ta sami yara ba.

Sai mala'kan yace wa Zakariya, "Matar ka zata sami yaro. Za ka sa masa suna Yahaya. Za'a cika shi da Ruhu Mai Tsarki, kuma zai shirya mutane domin Almasihu!" Zakariya ya amsa, "Matata da ni mun tsufa ainun har da zamu sami yara! Yaya zan san wannan zai faru?"

Sai mala'ikan ya amsa wa Zakariya, "Allah ne ya aiko ni, in kawo maka wannan labari mai dadi. Saboda ba ka gaskanta da ni ba, ba zaka iya yin magana ba har sai an haifi yaron. "Nandanan Zakariya ya kasa yin magana. Sai mala'ikan ya bar Zakariya. Bayan wannan, Zakariya ya koma gida matarsa kuma ta sami ciki.

Sa'anda Alisabatu tana da ciki wata shida, wannan Mala'ikan ba zato ya sake bayyana ga `yar'uwar Alisabatu wanda sunanta Maryamu. Ita budurwa ce wadda ke da alkwarin aure da wani nutum mai suna Yusufu. Sai mala'ikan ya ce, "Za ki yi ciki kuma ki haifi 'da. Za ki ba shi suna Yesu. Zai zama 'Dan Madaukaki Allah zai kuma yi mulki har abada."

Maryamu ta amsa, "Yaya wannan zai kasance da shike ni budurwa ce?" Mala'ikan yayi bayyani, "Ruhu Mai Tsarki zai zo gare ki, ikon Allah kuma zai lullube ki. Ta haka jaririn zai zama mai tsarki, 'Dan Allah." Maryamu ta gaskanta ta kuma amince da abinda Mala'kan ya fada.

Ba da jimawa ba bayan mala'ikan yayi magana da Maryamu, sai ta tafi ta ziyarci Alisabatu. Da jin muryar gaisuwar Maryamu, sai jaririn Alisabatu yayi tsalle a cikinta. Matan suka yi murna tare game da abinda Allah ya riga yayi dominsu. Bayan wata uku da Maryamu ta ziyarci Alisabatu, Maryamu ta koma gida.

Bayan Alisabatu ta haifi danta namaiji, Zakariya da Alisabatu suka ba jaririn suna Yahaya, kamar yadda mala'ika ya umarta. Sai Allah ya yarda wa Zakariya yayi magana kuma. Zakariya yace, "Yabo ga Allah, domin ya tuna da mutanensa! Kai, da na, za a kira ka annabin Madaukaki Allah wanda zai gaya wa mutane yadda zasu karbi gafara domin zunubansu!''

Verwandte Informationen

Worte des Lebens - GRN hat Audio-Gospel-Botschaften in tausenden von Sprachen, beinhaltet bibelbasierte Botschaften über die Erettung und das christliche Leben.

Freie Downloads - Hier findet man alle GRN Botschaften, Schriften in vielen Sprachen, plus Bilder und andere verwandte Materialien, verfügbar zum Download.

The GRN Audio Library - Evangelistic and basic Bible teaching material appropriate to the people's need and culture in a variety of styles and formats.

Choosing the audio or video format to download - What audio and video file formats are available from GRN, and which one is best to use?

Copyright and Licensing - GRN shares it's audio, video and written scripts under Creative Commons